Da Ɗumi-Ɗumi: Tsohon Ministan Noma Abba Sayyadi Ruma Ya Rasu

Labarin dake shigo mana yanzu daga Jihar Katsina na bayyana cewar, Allah ya yi wa tsohon Ministan noma Alhaji Abba Sayyadi Ruma rasuwa a birnin Landan na kasar Ingila bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.

Majiyar mu ta shaida mana cewa Alhaji Abba Sayyadi ya rasu a wata asibiti dake a birnin Landan bayan ya ziyarci asibitin domin a duba lafiyarshi.

Abba Sayyadi Ruma wanda aka haifa a ranar 13 ga Watan Maris shekarar 1962 ya rike mukamin sakataren Gwamnatin jihar Katsina daga bisani ya zama Ministan Noma da kula da ruwan Nijeriya a lokacin Marigayi Ummaru Musa Yar’adua.

Marigayin shine wanda ya assasa Makarantar Koyon kiwon lafiya dake a Batsari da Katsina watau Cherish College of Health Sciences.

Muna addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta mishi Allahumma Amin.

Labarai Makamanta

Leave a Reply